Uefa za ta binciki Barcelona kan sayen wasanni



Barcelona

Asalin hoton, Getty Images

Uefa za ta yi bincike kan Barcelona, sakamakon kudin da ta biya tsohon mataimakin shugaban kwamitin rafli a Sifaniya.

Tuni hukumar ta nada jami’in da zai yi bincike kan kudin da ake zargin Barcelona ta yi don ta samu sakamakon wasannin da zai amfane ta.

An shigar da karar Barcelona kan tuhumar cin hanci da bayar da rahoton karya da aikata rashin gaskiya.

Masu shigar da kara na tuhumar Barcelona da biyan fam miliyan 7.1 ga Jose Maria Enrique Negreira da kamfaninsa Dasnil 95.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like