Umarnin kotun kolin Najeriya a kan batun shari’ar daina amfani da tsoffin kudi ya jefa mutane cikin rudani



Kudi

Asalin hoton, Other

Masana shari`a a Najeriya, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu a kan umarnin da kotun kolin kasar ta bai wa bangarorin da ke shari’a a kan wa’adin da Babban Bankin kasar ya bayar na daina amfani da tsoffin takardun naira.

Masanan na ganin cewa umarnin kotun na da harshen damo ma’ana yana da sarkakiya.

Masanan sun ce rashin fayyace matsayin kowanne bangare da kotun ta yi shi ya sa suke kallon umarnin kotun a matsayin mai harshen damo.

Barista Sa’idu Muhammad Tudun Wada, lauya ne mai zaman kansa a Najeriya, ya kuma shaida wa BBC cewa, a yanzu ‘yan Najeriya sun shiga cikin rudani saboda rashin fayyace matsayin kowane bangare da kotun kolin ta yi, wanda haka zai sa jihohin da suka shigar da kara za su iya fassara umarnin kotun na kowa ya tsaya a matsayarsa har zuwa ranar da kotun za ta sake zama a matsayin umarnin hana dakatar da mutane daga mu’amala da tsoffin kudade.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like