Waiwaye: Ƙayyade farashin kujerar Hajji da ‘neman kotun Birtaniya ta sassauta wa Ekweremadu’



BBC ta yi waiwaye kan irin abubuwan da suka wakana tsakanin 1 zuwa 8 ga watan Afrilu ciki har da mutuwar mai ɗakin gwamnan Kano na farko da ɗage muƙabala da Sheikh Idris ‘kan zargin munana kalamai.

NAHCON ta sanar da kuɗin kujerar hajjin bana

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar kula da aikin hajji ta Najeriya NAHCON, ta sanar cewa maniyyata aikin hajjin bana za su biya kuɗi da ya kai naira miliyan biyu da dubu 890 a matsayin kuɗin kujera.

Shugaban hukumar Zikrullah Hassan, shi ya bayyan haka ranar Juma’a, inda ya ce matsalar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya da kuma Saudiyya a matsayin abubuwan da suka janyo ƙaruwar kuɗin hajjin bana.

Hassan ya ce farashin ya kai matakai takwas, inda jihohin Borno da Yobe suka kasance jihohi da za su biya kuɗi mafi ƙanƙanta yayin da Legas da Ogun za su biya kuɗi mafi girma da ya kai naira miliyan biyu da dubu 990.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like