Waiwaye: CBN ya ce ba zai ƙara wa’adi ba, wata mata ta auri saurayin ‘yarta a Kano



kudi

Asalin hoton, CBN

Babban bankin Najeriya CBN ya ce ba gudu ba ja da baya game da wa’adin da ya sanya na daina amfanin da tsoffin takardun kuɗin ƙasar daga ranar 31 ga watan Janairu.

Gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele ne ya bayyana haka cikin makon da ya gabata, bayan ganawar kwamitin babban bankin kan tsare-tsaren kuɗi.

Mista Emefiele ya jaddada cewa babban bankin ya bayar da wadataccen lokaci ga ƴan ƙasar da su mayar da tsoffin kuɗadensu zuwa bankunan ƙasar domin musanya su da sabbi.

Ya ƙara da cewa kawo yanzu babban bankin ya karɓi tsoffin takardun kuɗi da adadinsu ya kusa naira tiriliyan 1.5, tare da fatan cewa za su iya kai wa tiriliyan biyu kafin cikar wa’adin da bankin ya saka.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like