Waiwaye: Raɗe-raɗin kafa gwamnatin riƙon ƙwarya da naɗa shugaban riƙo na PDP



Abubuwa da dama ne suka faru a Najeriya a makon da muke ban kwana da shi, ciki har da cika shekara ɗaya da harin jirgin ƙasan Kaduna da naɗa shugaban riko na ƙasa da PDP ta yi.

DSS ta tabbatar da maƙarƙashiyar kafa gwamnatin riƙon ƙwarya

Asalin hoton, DSS/Facebook

A makon da muke yi wa bankwana ne, Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya, DSS, ta ce ta shaida wasu jiga-jigai da ke kitsa wata maƙarƙashiya don kafa gwamnatin riƙon ƙwarya a ƙasar.

Hukumar ta ce maƙarƙashiyar, wadda wasu ke izawa ba kawai aba ce da ta saɓa wa doka ba, wani ƙoƙarin masu jamhuru ne na kifar da tsarin mulkin Najeriya da kuma jefa ƙasar cikin wani rikici da za a iya kauce masa.

Ta ce tunanin kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, abu ne da ba za a amince da shi ba, a tsarin dimokraɗiyya da kuma muradin zaman lafiyar al’ummar ƙasar.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like