Waiwaye: Yajin aiki kan farashin mai da kuma alƙawuran Tinubu bayan zama shugaban ƙasa



Wannan maƙalar na ɗauke da muhimmai daga cikin abubuwan da suka faru a Najeriya a makon da muke bankwana da shi.

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC za ta shiga yajin aikin sai-baba-ta-gani a Najeriya

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

‘Yan ƙwadago a Najeriya

Kungiyar kwadago a Najeriya ta NLC ta ce za ta fara yajin aiki na gama-gari daga ranar Laraba, 7 ga watan nan na Yuni sakamakon matakin gwamnati na cire tallafin man fetur.

Shugaban kungiyar Joe Ajaero shi ne ya sanar da haka, bayan wani taron gaggawa da shugabannin kungiyar suka yi ranar Juma’a a Abuja.

Kwamared Ajaero ya ce gwamnati musamman ma kamfanin mai na NNPC na da wa’adin zuwa Laraba ya mayar da farashin man fetur kamar yadda yake a da idan ba haka ba za su shiga yajin aikin sai-abin-da-hali-ya-yi da kuma zanga-zanga a fadin kasar.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like