Wani Dan Majalisa Ya Arce Da Sandan Iko Na Majalissar Dokokin Jihar Gombe


Rahotanni daga jihar Gombe sun tabbatar da cewa dan majalisar dokokin Gombe mai wakiltar Akko ta Yamma, Hon. Abdullahi Abubakar ya arce da sanda iko na majalisar dokokin a lokacin da ake yunkurin tsige Shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hon. Mohammed Haruna.

A ranar 5 ga watan Mayu ne dai, Shugaban Marasa Rinjayen ya kira taron manema Labarai inda ya nuna cewa an yi rashin adalci a zaben Shugabannin jam’iyyar APC na jihar, wanda a kan haka wasu suka nemi a tsige shi amma kuma ‘yan Majalisa hudu daga cikin su takwas na APC ba su goyi bayan hakan ba.

You may also like