Wasa ukun da ke gaban Super Eagles don zuwa kofin Afirka



Super Eagles

Asalin hoton, Super Eagles

Super Eagles za ta buga wasa na hudu a rukunin farko a gidan Guinea Bissau ranar Litinin, domin neman shiga gasar kofin Afirka.

Wasa na biyu kenan da Super Eagles za ta kara da Guinea Bissau, wadda ta doke ta 1-0 ranar Juma’a a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, Najeriya.

Daga nan Super Eales za ta buga wasa na biyar a cikin rukuni ranar Litinin 12 ga watan Yuni, inda za ta karbi bakuncin Saliyo.

Ranar Litinin 4 ga watan Satumba, Najeriya za ta karbi bakuncin Sao Tome a wasa na shida na karshe a rukunin farko.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like