Gwamnatin jihar Taraba ta tabbatar da cewa za ta bi sahun jihar Binuwai wajen kaddamar da dokar hana kiwo a jihar.
Kwamishinan shari’a na jihar ya bayyana cewa bin matakin kafa dokar ya zama dole ganin yadda gwamnatin tarayya ta kasa daukar matakin da ya dace wajen cafko wadanda suka kai harin Binuwai.