Wuraren da za a ci gaba da zaɓen gwamna a ranar Lahadi



...

Asalin hoton, Getty Images

A Najeriya hukumar zaɓen ƙasar ta ce za a gudanar da zaɓen gwamnan da na majalisar dokokin jihohi a wasu yankuna na ƙasar ranar Lahadi.

Hukumar ta ce hakan zai faru ne kasancewar ba a samu gudanar da zaɓen a irin waɗannan mazaɓu ba.

A wata sanarwa da ta fitar, hukumar zaɓe a jihar Rivers da ke kudancin ƙasar ta an ɗage zaɓen a ƙaramar hukumar Asari-Tobu da kuma gunduma ta 14 a ƙaramar hukumar Degema.

Sanarwar da hukumar INEC ta fitar ta ce ba a samu gudanar da zaɓen a waɗannan yankuna ba kasancewar masu kaɗa ƙuri’a sun turje wa ma’aikatan da aka tura.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like