Wutar lantarki sun tozarta Ministan wuta da aikace aikace kuma tsohon gwamnan jihar lagos a dai dai lokacin dayake tsaka da bayani akan wutar lantarkin a otel eko dake jihar lagos.
Fashola yana cikin bayani akan karuwar karfin wutar a nijeriya da kuma shirye shiryen da suke na ganin wutar ta ci gaba da karuwa, kwasam sai aka dauke wuta a otel din da yake maganar inda hakan ya karyata maganar da yake fada akan tsayuwar wutar lantarkin a Najeriya.