Wutar lantarki ta kashe mutum 10 a Zaria



.

Asalin hoton, Getty Images

Mazauna Unguwar Gwargwaje da ke birnin Zaria a jihar Kaduna a arewacin Najeriya sun gamu da wani iftila’i bayan da wutar lantarki mai karfi ta yi sanadiyyar mutuwar mutum goma.

Kazalika lamarin ya jawo ƙonewar gidaje masu yawa ƙurmus.

Mazauna unguwar sun ce lamarin ya auku ne cikin daren Laraba yayin da suke barci bayan da aka mayar da lantarki a yankin.

Wannan lamari ya jefa al’ummar Unguwar Gwargwaje cikin yanayi na damuwa bayan da suka wayi garin Laraba babu wasu cikin matansu da ‘ya’yansu da kuma iyayensu.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like