Ya Kashe Kansa Saboda Zargin Sa Da Satar Wayar Salula


Sunansa Adamu da safiyar yau ya rataye kansa bayan da abokansa suka tuhume shi da satar waya. Lamarin da ya haifar da rigima a tsakanin su. Marikiyarsa ta shaida wa majiyar Arewa24news cewa Marigayin dan asalin garin Misau ne da yazo neman kudi garin Jimeta a jahar Adamawa.

Marigayin ya aikata aika-aikar aika ruhin sa zuwa kiyama ne a unguwar Bauchi Street dake garin jimeta fadar mulkin jahar Adamawa. A yayin daukar wannan rahoto, jami’an tsaro suna shirin daukar gawar.

You may also like