‘Yadda aka dakile yunkurin juyin mulki a kasar Gambia’



Shugaba Adama Barrow

Asalin hoton, Getty Images

Gwamnatin kasar Gambia ta ce ta dakile wani yunkurin juyin mulki.

An kama sojoji hudu sannan mutum uku da ake zargi da taimaka musu sun tsere, a cewar wata sanarwa da gwamnati ta fitar.


Babu cikakken bayani game da hakikanin abin da ya haddasa yunkurin juyin mulkin na ranar Talata da zummar kifar da gwamnatin Shugaba Adama Barrow, wanda ya yi nasara a zabe karo na biyu a shekarar da ta gabata.

An san Gambia a matsayin kasar da ake kwanciyar hankali inda masu yawon bude ido ke tururuwa cikinta domin kallon namun daji da hutawa a bakin tekuna.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like