Yadda India ta taso keyar ‘yan Najeriya 196 zuwa gida



Police for Delhi, India arrest two Nigerians wit one lady from Kenya ontop suspicion say dem be drug supplier

Asalin hoton, Getty Images

Kasar Indiya ta taso keyar wasu ‘yan Najeriya kusan dari biyu da sauka hada da maza da mata da kananan yara zuwa gida, sakamakon rashin gamsuwa da yanayin zamansu a kasar ta Indiya.

A maraicen jiya Juma’a ne hukumomin Najeriya suka karbi wadannan mutane a Abuja, babban birnin tarayyar kasar, wadanda hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasar, wato NEMA, ta yi dawainiyar kwaso su daga Indiyar.

Bashir Idris Garga, babban jami’in kai dauki na hukumar ta NEMA, ya yi wa BBC karin bayani.

“Akwai wasu ‘yan Najeriya da ke zaune a Indiya, wadanda hukumomin kasar ba su gamsu da zamansu ba, ko kuma sun zama musu damuwa a kasar. Wannan ne yasa suka bukaci gwamnatin Najeriya ta gaggauta dawo da su gida.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like