Yadda ‘yan Najeriya suka shiga rudani a kan ci gaba da amfani da tsoffin kudi ko kuma a’a



Kudi

Asalin hoton, Other

Al’ummar Najeriya sun shiga rudani na ko su ci gaba da amfani da tsofaffin kudin kasar ko kuma a’a.

Rudanin dai ya samo asali ne daga Babban Bankin kasar CBN da kuma gwamnatin tarayya bayan da suka yi gum a kan ko za su bi umarnin kotun kolin kasar na a kara wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi ko kuma a’a.

Da dama daga cikin al‘ummar kasar sun bayyana damuwarsu ta rashin sanin matsayar da aka cimma.

Wasu mutane da BBC ta zanta da su sun ce tun da ranar da wa’adin da CBN din ya kara na amfani da tsoffin kudin ta cika wato 10 ga watan Fabrairun 2023, gidajen mai da wasu shagunan ‘yan kasuwa suka daina karbar tsoffin takardun kudi, sai su ce wai ai an ce a daina amfani da su.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like