Ya Kamata Jam’iyyar APC Ta Hukunta Gwamnan El-rufai Saboda Wasikar Da Ya Rubuta Na Kalubalantar Gwamnatin Buhari, Cewar Shehu Sani
Sanata Shehu Sani, ya kara da cewa a duk lokacin da ya ga kuskure a gwamnatance, da zarar ya fadi albarkacin bakinsa, sai gwamna Elrufai ya nemi jam’iyya ta hukunta shi kan kalaman da ya yi, don haka ne a yanzu shi ma ya yi kira ga jam’iyyar ta APC da ta hukunta gwamnan saboda kalaman nasa.