‘Yan Fashin Shanu A Zamfara Sun Mika Makamansu. 


Wasu ‘yan fashin shanu a kananan hukumomin, Birnin Magaji,Maru da Gusau dake a jihar zamfara sun mika makamansu ga rundunar soji dake jihar.

Mai magana da yawun hukumar soji ta kasa,  birgediya janar, sani usman ya shaidawa manema labarai haka yau a Abuja.

Usman yace  makaman masu hatsarine kwarai dagaske, wadanda suka hada da bindiga samfurin   G3 , da na gargajiya 434, dakuma kanana samfurin fistol 69.

An dai mika mkaman ne dai ga rundunar soji ta 233 bataliya ta daya, a idon makarraban gwamnatin jihar.

You may also like