Yan mata Chibok 13 ne suke a raye cikin 113 dake tsare a hannun Boko Haram – Ahmad Salkida


Ahmad Salkida shahararren danjaridar nan dake samun labarai daga shugabannin kungiyar Boko Haram ya ce 15 ne kacal suke a raye daga cikin yan matan Chibok 113 dake tsare a hannun Boko Haram.

Salkida wanda ya bayyana haka cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya ce da yawa daga cikin yan matan sun mutu sakamakon musayar wuta tsakanin sojoji da yayan kungiyar ta Boko Haram a lokacin da sojojin suka yi kokarin ceto su.

Yau shekara hudu kenan tun bayan da aka sace yan matan su 276 daga makarantar sakandaren yan mata dake Chibok a jihar Borno.

Ya yin da 163 suka dawo hannun iyayensu an yi ittifakin cewa ragowar yan matan 113 na can tsare a hannun Boko Haram.

Amma Salkida ya ce ragowar yan matan da suke a raye basa hannun shugaban kungiyar, Abubakar Shekau.

A cewarsa an aurar da su inda ya ce mazajensu ne kawai za su iya yanke makomarsu.

Ya kara da cewa tattaunawa ko kuma biyan kudin fansa ba zai sa a saki yan matan ba sai dai idan har mazajensu sun sake su.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like