Jagoran Jam’iyyar APC na kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, Najeriya na bukatar mutum irin tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar domin inganta rayuwar ‘yan Najeriya.
A wata Wasikar taya murnar cikar Atiku shekaru 70 da haihuwa wacce Tinubu ya aika masa, ya bayyana Turakin Adamawa a matsayin mutum mai Imani, wanda Imanin sa ne ya sa shi rayuwa cike da kwazo gami da cikakkiyar lafiya.