Wasu daga cikin ya’yan kungiyar yan uwa Musulmi da aka fi sani da Shi’a sun gudanar da zanga-zanga inda suka kona tutar kasar Amurka da kuma ta Isra’ila a birnin tarayya Abuja ihakan ya jawo zaman d’ar-d’ar a birnin.
Suna tafiya tare da rera wakoki da kada tuta mabiya akidar ta shi’a sun ce suna zanga-zanga ne kan yan kungiyar da aka kashe a yankin Falasɗinu.
Zanga-zangar ta fara ne daga babban masallacin Abuja ya zuwa shatale-talen Julius Berger dake birnin.
Yan sanda dauke da makamai sun ja tunga a wasu muhimman wurare domin hana karyewar doka da oda.
Masu zanga-zangar na dauke da allunan dake allawadai da kasar Amurka da kuma neman a saki Zakzaky da kuma samawa da kasar Falasɗinu yanci.
Daga bisani mutanen sun tattara karkashin gada inda suka kona tutar kasar Amurka da ta Isra’ila.
Zanga-zanga ta haifar da tsaiko ga zirga-zirga ababen hawa dama ta mutane akan hanyar kasuwar Wuse dake birnin.