‘Yansanda sun tabbatar da mutuwar ‘yan Ƙunar baƘin wake 2 a Borno


‘Yansanda a jIhar Borno a yau lahadi sun tabbatar da mutuwar ‘yan kunar bakin wake maza 2 a Maiduguri.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandar jihar Mr Victor Isuku a jawabinsa a Maiduguri yace harin farko ya farune a garejin Muna dake kusada ƙofar shigowa garin inda maza ‘yan ƙunar bakin wake biyu suka rasa rayukansu.

” A yau misalin 4:38, mutane ‘yan kunar bakin wake suka sa bam a jikinsu kusa da garejin Alhaji Bukar Gujari dake Muna a ƙofar shigowa gari.”

Isuku yace duk ‘yan ƙunar bakin waken sun mutu  ,yace bam din yayi fata-fata da motar da aka aje kusa dasu.

Sannan Isuku ya ƙara da cewa bam yatashi a ƙauyen dasuna inda ya kashe mai sanye da bam ɗin sannan ya jiwa mutum 1 rauni.

You may also like