Harin Saudiyya A birnin Sanaa.
Jiragen yakin Saudiyya sun kai hari a babban birnin kasar Yeman, San’aa.
Haren-haren na jiragen saudiyya sun shafi yankin Bani Bahlul a cikin babban birnin. Fararen hula da dama ne su ka rasa rayukansu sanadiyyar harin, wasu kuma da dama suka jikkata.
A gefe daya, sojojin kasar da kuma dakarun sa kai na Ansarulla, sun maida martani ya hanyar kai hari a sansanonin sojojin Saudiyya a kudancin kasar.
Fiye da watanni 20 kenan da Saudiyya ta shelanta yaki akan kasar Yeman da al’ummarta wanda kawo ya zuwa yanzu ya ci dubban rayuka.