Zaɓen 2023: Amnesty ta aike da gargaɗi mai karfi kan razana masu zaɓe



Zaben Najeriya

Asalin hoton, Getty Images

Ƙungiyar Amnesty International ta ce dole ne hukumomin Najeriya da jam’iyyun siyasar ƙasar da ‘yan takara su fito fili su yi alla-wadai da masu kalaman nuna ƙiyayya da tunzura tashin hankali da kuma razana masu zaɓe.

Ta ce ba za a lamunci yadda wasu ‘yan siyasa da idonsu ya rufe, ke ingiza tashin hankali da neman a kai wa abokan hamayya hare-hare a lokutan yaƙin neman zaɓe ba.

Amnesty na wannan kira ne, kwanaki kaɗan a fita rumfunan zabe domin kada kuri’ar zaɓen shugaban ƙasa.

‘Gazawar hukumomi’

Ƙungiyar Amnesty International ta ce gazawar hukumomi wajen gurfanar da mutanen da suka tunzara miyagun rikice-rikice a zaɓukan baya a kotu, ta haifar da wani yanayi na aikata laifi da gadara da kuma zuga wasu.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like