Zaɓen 2023: Ba dai masu zaɓe su tsaya jiran kayan aiki ba wannan karo – INEC



.

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa a Najeriya, ta yi alƙawari cewa a zaɓen 2023, kayan aiki ne za su jira masu zaɓe a rumfunan kaɗa ƙuri’a saɓanin yadda aka dinga samu a baya.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmoud Yakubu ne ya shaida hakan yayin wani taro don ƙulla yarjejeniya da ƙungiyoyin sufuri na NURTW da NARTO kan hanyoyin sauƙaƙa jigilar ma’aikata da kayan aikin zaɓe zuwa cibiyoyin zaɓe.

A cewar shugaban hukumar, sun yi waiwaye kan matsalolin da aka dinga fuskanta a zaɓen 2019, kuma hakan ya sanya su ɗaukar matakan riga-kafi daga manyan ƙalubalen da za su iya kawo cikas ga nasarar zaɓen shekara mai zuwa.

Ya ce hakan ba zai yiwu ba har sai INEC ta samu ƙarin motoci da babura da kwale-kwale musamman a yankunan da ke kusa da ruwa, inda isar ma’aikatan hukumar zuwa waɗannan wuraren a kan lokaci ke da wahala.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like