Zaɓen 2023: “Na tuba da banga abin da ‘yan siyasa ke ba mu ko abinci ba zai saya ba”



.

Wani abu da ake zargin ‘yan siyasa da mayar da hankali a kai a duk lokacin da aka kaɗa gangar siyasa kuma aka fara yaƙin neman zaɓe shi ne amfani da ‘yan bangar siyasa.

‘Yan siyasar dai kan yi amfani da kuɗaɗen a wani lokaci ma ba su taka kara sun karya ba, tare da bai wa matasa ƙwaya don yin amfani da su wajen illata abokan adawa ko kuma tayar da tarzoma a lokutan zaɓe.

To sai dai matasan sun fara karatun ta-nutsu inda aka fara samun wasu suna tuba tare nadamar abin da suka yi a baya, har ma sun shiga fafutukar janyo hankulan takwarorinsu waɗanda har yanzu ba su ritaya daga bangar siyasa ba.

Sagiru Yerima, na ɗaya daga cikin ‘yan bangan da a yanzu suka tuba har ma ya fara jagorantar gangami don tabbatar da ganin an gudanar da zaɓen 2023 ba tare da banga ba a jihar Kano.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like