A ranar 18 ga watan Janairu ne al’ummar Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnoni a jihohi 28, da kuma na majalisar dokokin jiha a faɗin ƙasar.
Adamawa na da yawan mutanen da suka yi rajistar zaɓe 2,196,566.
Mutum goma sha biyar ne ke takarar kujerar gwamnan, ciki har da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jam`iyyar da Sanata Aishatu Dahiru Binani ta jam`iyyar APC, da Umar Ardo na jam`iyyar SDP da kuma Mohammed Usman Shuwa na jam`iyyar ADC.