Za a ci gaba da wasannon Premier League daga ranar Asabar



Marinelli

Asalin hoton, Getty Images

Ranar Asabar 11 ga watan Fabarairu za a ci gaba da wasannin mako na 23 a gasar Premier League, inda za a yi karawa bakwai.

Kawo yanzu an buga karawa 210 an kuma ci kwallo 576, kuma Erling Haaland na Manchester City shi ne kan gaba a zura kwallaye a raga mai 25.

Cikin wasannin da za a buga ranar Asabar Arsenal wadda take jan ragamar teburin a bana mai maki 50 za ta karbi bakuncin Brentford a Emirates, wadda take ta bakwai mai maki 33.

Za a fara ne da karawar West Ham United da Chelsea da tsakar rana, inda kungiyar David Moyes take ta 17 da maki 19.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like