Za a kafa sabuwar gwamnati a kasar Austriya


 

Jam’iyyar masu ra’ayin rikau a Austriya tare da jam’iyyar masu kyamar baki sun gabatar da yarjejeniyar da suka cimma ta kafa gwamnati ga shugaban kasar Alexander Van der Bellen.

41818606_303

Sebastian Kurz ministan harkokin waje wanda jam’iyyarsa ta ÖVP ta samu nasara a zaben ‘yan majalisun dokoki a watan Oktoba. Ya bude shawarwari da jam’iyyar masu kyamar baki ta FPÖ ta Heinz Christian Strache don samun rinjaye don kafa gwamnati. A shekara ta 2000 kungiyar tarrayar Turai ta sakawa Austriya takunkumin karya tattalin arziki bayan da jam’iyyar masu kyamar bakin ta shiga gwamnati.

You may also like