Za mu nemi madadin Jesus a Janairu- Arteta



Arteta

Asalin hoton, OTHER

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya ce za su shiga kasuwa a watan Janairu, biyo bayan raunin dan wasan gabansu Gabriel Jesus.

Jesus ya ci wa Gunners kwallaye biyar ya kuma taimaka aka ci shida a kakar bana a gasar Premier League kafin aje hutun Qatar 2022.

Sai dai mai shekaru 25 din ya samu rauni a lokacin da yake wakiltar kasarsa a gasar kofin duniya da aka kammala a Qatar.

Tuni an yi wa Jesus aiki, kuma zai shafe lokaci kafin ya dawo fagen daga.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like