Zaben 2023: An ba ‘yan agaji 500 horo domin inganta tsaro a Najeriya



..

An kawo karshen bayar da horo na kwanaki hudu a Abuja babban birnin Najeriya ga wasu ‘yan agaji game da irin rawar da za su taka wajen inganta tsaro a wuraren da ke da cinkoson jama’a domin kare rayuwarsu da dukiyoyinsu, musamman ma a lokacin babban zaben kasar da ke tafe.



A watan Fabrairun shekara mai zuwa ne dai ake sa ran gudanar da babban zaɓen a fadin ƙasar.

An horar da ‘yan agaji fiye da 500 ne daga kungiyoyi bakwai na addinin Islama na sassan Najeriya daban-daban.



Daya daga cikin wadanda suka shirya wannan taron horaswan shi ne Abdullahi A. Diggi – babban jami’in bayar da agajin gaggawa a kungiyar Izala ta kasa a Najeriya.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like