Zaben gwamnan Ondo: APC ta bai wa PDP tazara mai yawa


Sakamakon zaben jihar Ondo da ke kudancin Najeriya da hukumar zaben INEC ta fitar ya zuwa yanzu ya nuna cewa jam’iyyar APC mai mulki ce a kan gaba.

Zuwa yanzu, INEC ta fitar da sakamakon zaben kananan hukumomi 12 cikin 18, abin da ya nuna cewa APC ta lashe zaben kananan hukumomi tara yayin da PDP ta yi nasara a kananan hukumomi uku.

Gwamna Rotimi Akeredolu shi ne kan gaba a zaben yayin da dan takarar jam’iyyar PDP Eyitayo Jegede yake biye da shi.

Kananan Hukumomi:

Akoko North-West – APC: 15, 809 – PDP: 10,320

Akoko North-East – APC: 16,572 – PDP: 8,380

Akoko South-East – APC: 9,419 – PDP: 4,003

Akoko South-West – APC: 21,232 – PDP: 15,055

Ifedore – PDP: 11,852 – APC:9,350

Akure North – PDP: 12,263 – APC: 9,546

Ile-Oluji/Okeigbo – APC: 13,278 – PDP: 9,231

Akure South – PDP: 47,627 – APC: 17,277

Owo – APC: 35,957 – PDP: 5,311

Idanre – APC: 11,286 – PDP: 7,499

Ondo East – APC: 6,485 – PDP: 4,049

Irele – APC: 12,643 – ZLP: 5,904

You may also like