Zaben Najeriya na 2023: ‘Na fid da rai ga ‘yan siyasa tun bayan rasa mahaifina da dukiyata a hare-haren ‘yan bindiga’



  • Marubuci, Umaymah Sani Abdulmumin
  • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multimedia Broadcast Journalist
  • Twitter,
'yan takarar shugabancin Najeriya na 2023

Asalin hoton, Others

“Zuciyata na ƙuna, ina tunanin yaushe zan sake ganin farin ciki a rayuwata, mutuwar mahaifina ita ce ta fi ɗaga mun hankali, ga shi na rasa komai a rayuwa”, kalmomin Mu’azu Kabir Baso da harin ‘yan bindiga ya tarwatsa danginsa da raba su da muhallansu kenan.

Mu’azu Kabir Baso matashi ne kuma magidanci mai shekara 28 a duniya, da a kullum ya ke zub da hawaye duk lokacin da ya tuna yanayi na uƙubu da ya tsinci kansa sakamakon matsalolin tsaro a Najeriya.

Mu’azu wanda asalinsa ɗan jihar Katsina ne, ya ce ya rasa mahaifinsa da ‘yan uwa a wani ƙazamin hari da aka kai wa gidansu a karamar hukumar Sabuwa ta Katsina.

Mutumin, magidanci ne mai yara biyu, kuma ya shaida mana irin asarar da ya tafka a cikin lokaci kalilan na rayuwarsa, da kuma wahalhalun rayuwa da sabbin nauye-nauyen da ya faɗa a kansa.





Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like