Zaben Najeriya na 2023: ‘Yadda muka kafa kwamiti don magance matsalar tsaro a garinmu’



.

Asalin hoton, others

Al’ummar garin Kalmalo a yankin ƙaramar hukumar Illela a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya sun kafa wani kwamiti domin magance matsalar tsaro a garinsu.

Al’ummar garin sun ce kasancewar batun samar da tsaro yana nema ya yi wa gwamnati yawa sakamakon yawaitar tashe-tashen hankulan da wasu yankunan ƙasar ke fuskanta.

Wannan ne dalilin da ya sa suka haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen kafa kwamitin inda masu kuɗi da masu mulki da manoma da ‘yan kasuwa da talakawa suka haɗa kai wajen samar da wannan kwamiti.

Wani mazaunin garin mai suna Safiyanu Abubakar ya ce kwamitin na aiki ”ba dare da rana wajen tabbatar da tsaro a garinmu, domin ana gadi, ana kula da shige-da-ficen jama’a a faɗin garinmu”.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like